Tun daga karshen watan Afrilu, 'yan jarida fiye da dubu dari daya suka soma fama da aiki kan bikin baje kolin. A kullum cibiyar watsa labaru dake farfajiyar bikin na bude kofa ga wadannan 'yan jarida daga Sin da kasashen ketare. Wasu 'yan jarida na kasashen ketare kuma suna mayar da cibiyar a matsayin tamkar gidansu.
Mao Jie, daraktar tashar manema labaru ta jaridar Ta Kung Pao ta Hongkong dake birnin Shanghai ya bayyana cewa, kofi da cibiyar watsa labaru take bayarwa ya burge shi sosai, a ranar dake da yanayin zafi kuma, a kan gabatar da ruwan da aka sanya kankara a ciki. Ban da wannan kuma, masu ba da hidima su kan tashi daga cibiyar watsa labaru bayan da 'yan jarida suka kammala ayyukansu. Yanzu, 'Al'adun kofi' ya zama alamar musamman ta cibiyar, 'yan jarida na gida da na kasashen ketare dukkansu sun gamsu da wannan hidima.