Malam Chen Zhu ya bayyana cewa: " bikin murnar ranar rumfar kasar Gabon ya ba mu wata dama wajen fahimtar al'adun kasar Gabon da wurare masu ban sha'awa na kasar."
Ban da haka kuma, malam Chen Zhu ya jaddada dankon zumunci da ke tsakanin kasashen biyu. Inda ya bayyana cewa, " tun shekaru 36 da suka wuce da kafa dangantakar diplomasiyya a tsakanin kasashen biyu zuwa yanzu, bisa kokarin da shugabannin kasashen biyu suka yi, dangantakar da ke tsakanin kasahen biyu ta samu bunkasuwa sosai. Shugabannin kasashen biyu sun yi mu'amala da yawa, da ci gaba da kara fahimtar juna a fannin siyasa, kuma an samu sakamako mai kyau wajen yin hadin gwiwa a fannonin tattalin arziki da ba da ilmi da kiwon lafiya, kasashen biyu sun yi hadin gwiwa wajen warware batutuwan kasa da kasa. A ganina, bikin EXPO zai ci gaba da kara fahimtar juna da ke tsakanin jama'ar kasashen biyu, da samar sabuwar damar na bunkasuwar dangantakar da ke tsakaninsu."