A watan Agusta na shekarar 2008, Mr. Ramos-Horta ya halarci bikin bude wasannin Olympics na Beijing bisa gayyatar da aka yi masa. Ya bayyana cewa, dalilan da suka sa kasar Timor ta gabas halartar bikin EXPO cikin nasara su ne, da farko ta samu goyon baya daga kasafin kudi na kasar, na biyu shi ne, ta samu taimako daga wajen kasar Sin. Wannan ya nuna kyakkyawar dangantaka dake tsakanin kasashen biyu. A yayin da yake tabo zancen bunkasuwar wannan dangantaka, Ramos-Horta ya bayyana cewa, 'Kasashen Timor ta gabas da Sin suna kokarin bunkasa dangantakar dake tsakaninsu yadda ya kamata. Dangantakar tsakanin kasashen biyu ta cancanci misali, kuma abun koi na dangantaka tsakanin kasa da kasa, tsakanin gwamnatoci, da kuma tsakanin jama'a. Kasar Sin ta ba mu tallafi a fannonin al'adu, da tsaron kasa, da sauransu. Lallai mun gamsu da hadin gwiwa da ake yi tsakanin kasashen biyu.'