in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Muna fatan kasashen duniya za su kara fahimtar kasar Timor ta gabas ta bikin EXPO na Shanghai, a cewar shugaban kasar
2010-07-14 15:57:02 cri

Ranar 13 ga wata, rana ce da aka fi samar da nune-nune a rumfar kasar Timor ta gabas, wannan ne kuma karo na farko da kasar ta halarci bikin baje koli na duniya bayan da ta samu 'yancin kai a shekarar 2002. Kwanan baya, a yayin da yake ganawa da manema labaru, shugaban kasar, Jose Ramos-Horta ya bayyana cewa, yana fatan kasashen duniya za su kara fahimtar kasar Timor ta gabas ta wannan bikin baje koli na Shanghai.

A ranar 11 ga wata, Mr. Ramos-Horta ya iso birnin Shanghai, don halartar bikin murnar ranar nune-nune na rumfar kasar. Ya ce, ko da yake na iso birnin Shanghai ba da dadewa ba, amma ko da haka birnin ya sheda kyakkyawar alamar bunkasa kan tattalin arziki. Ya kara bayyana cewa, 'Birnin Shanghai ya ba ni kyakkyawar sura a zuciyata. Birnin Shanghai kuma zai zama wani birnin da ya fi zama na zamani a duniya, da kuma wata cibiyar da ta fi girma a fannin hada-hadar kudi a duniya.'

Bayan haka kuma, shugaban kasar Timor ta gabas, Jose Ramos-Horta ya bayyana cewa, yana fatan ta hanyar bikin baje koli na duniya, mutane daga kasashe daban daban za su kara fahimtar yanayin da kasar Timor ta gabas ke ciki. Ya kara da cewa, 'Muna jin farin ciki sosai don halartar wannan biki a matsayinmu na wata sabuwar kasa. Wannan ne kuma karo na farko da muka halarci bikin EXPO bayan da muka samu 'yancin kai. Na yi imani cewa, masu yawon shakatawa da suka fito daga kasar Sin da sauran kasashe za su kara fahimtar yanayin da kasar Timor ta gabas ke ciki, da al'adu da tarihinmu, da kuma ci gaban da muka samu.'

1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China