Ngamse Tsering, wani dan kabilar Tibet da iyalansa 13 suka mutu sakamakon bala'in ya gaya wa wakilinmu cewa, zai yi tawakkali da kokarin samun kwarin gwiwa wajen sake sabon zaman rayuwarsa. Ya ce, "Yanzu abu mafi muhimmanci shi ne yin tawakkali da samun kwarin gwiwa wajen ci gaba da zaman rayuwa. Mun gode wa gwamnatinmu, da abkuwar girgizar kasa, ta kawo mana tantuna da abinci da abin sha ba tare da bata lokaci ba."
Ban da wannan kuma, a makarantu da filaye da unguwanni na wurare daban daban na kasar Sin, jama'a na kabilu daban daban sun nuna alhini ga mutuwar mutane ta hanyar samar da furanni da kudin taimako da yin fatan alheri.(Kande Gao)