Ban da wadannan kuma, Xu Jinghu ta ce, kasar Morocco ta mai da muhimmanci sosai kan ziyarar Yang Jiechi, kuma bangarorin biyu sun yi shawarwari cikin sahihanci da jituwa. Hakan ya bayyana abokantaka mai dorewa kuma ta gargajiya dake tsakanin Sin da Morocco. Ana sa ran cewa, kasashen biyu za su karfafa hadin gwiwarsu a fannonin tattalin arziki da ciniki da zuba jari da kuma sauransu a karkashin tsarin dandalin tattaunawa na hadin gwiwa dake tsakanin Sin da kasashen Afrika ta yadda za a samu damar bunkasa huldar dake tsakanin Sin da Morocco a dukkan fannoni.(Lami)