in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bukaci kasashen Afrika su yi wa dokokin tsara birane garambawul
2019-05-31 09:58:36 cri
MDD ta bukaci gwamnatocin kasashen Afrika da su yiwa dokokin tsara birane garambawul domin su dace da tsarin cigaba na yanayin da ake ciki a halin yanzu.

Robert Lewis-Lettington, shugaban sashen tsara dokoki na hukumar raya birane ta MDD ya bayyana hakan, yace a mafi yawan kasashen Afrika dokaki ba sa aiki, ya fada a lokacin kaddamar da littafi mai taken muhimmancin tsara dokoki a yankin dake kudu da hamadar saharar Afrika (SSA) a lokacin taron raya birane na MDD wato UN Habitat wanda ke gudana a Nairobi.

Ya bayyana cewa, daga cikin kasashen Afrika 18 da aka yi samfurinsu a shiyyar, birnin Johannesburg na kasar Afrika ta kudu ne kadai ya yi cikakken aiwatar da tsarin, yayin da a kasashe mafi yawa tsarin dokokin ba ya aiki.

Lewis Lettington ya ce, ana aiwatar da kashi 85 bisa 100 na dokokin tsara birane ne a helkwatocin mulki na kasashe, yayin da ake aiwatar da kashi 38 bisa 100 na dokokin a sauran birane.

"Hukumar UN-Habitat ta riga ta taimakawa kasashe tare da taimakon gwamnatocin kananan hukumomi da gwamnatin tsakiya na kasashen, " in ji shi. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China