in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalissar rikon kwarya a Sudan ta sallafi wasu alkalai
2019-04-17 10:00:37 cri

Majalissar gudanarwa ta rikon kwarya ta kasar Sudan, ta sallafi wasu alkalai daga bakin aikin su, a wani bangare na biyan bukatun da masu zanga zanga suka nema, bayan hambarar da gwamnatin tsohon shugaban kasar Omar Al-Bashir a makon jiya.

Wata sanarwa da majalissar ta fitar a jiya Talata, ta ambato jagoran majalissar ta soji Abdel-Fattah Al-Burhan, yana bayyana sallamar babban mai shari'a Omer Ahmed Mohamed Abdel-Salam, da mataimakin babban mai gabatar da kara na kasar Husham Osman Ibrahim, da mai gabatar da kara Amer Ibrahim Majid. Kaza lika sanarwar ta bayyana Al-Waleed Sid-Ahmed Mahmoud, a matsayin sabon babban mai shari'ar kasar.

Majalissar gudanarwa ta rikon kwarya wadda sojoji ke jagoranta ce ke jan ragamar kasar Sudan a halin yanzu, ko da yake fararen hula masu bore, na ci gaba da zaman dirshan a sassan kasar, a wani mataki na matsin lambar ganin an mika mulki ga zababbiyar gwamnatin farar hula.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China