in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan jaridar kasashen Afirka: ba za a iya lalata hadin kan Sin da Afirka ba
2019-03-09 17:34:41 cri

A yayin taron manema labaru da aka shirya a jiya Juma'a game da zaman taro na biyu na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin karo na 13, ministan harkokin wajen kasar Wang Yi ya amsa tambayoyin manema labaru na ciki da wajen kasar Sin, kan manufofin diplomasiyyar kasar da alakar dake tsakaninta da kasashen ketare. Game da haka, 'dan jarida Ongango Victor daga jaridar Daily Nation ta kasar Kenya da Deo Kamagi daga jaridar Daily News ta kasar Tanzaniya suka bayyana cewa, bayanin da minista Wang Yi ya yi kan dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen Afirka ya kara musu kwarin gwiwa, domin ana gudanar da hakikanin hadin kai tsakanin bangarorin biyu, suna cewa babu wasu munanan ra'ayoyin ciki har da "Sabon salon mulkin mallaka " da ka lalata dangantakar.

'Dan jarida Ongango Victor ya bayyana cewa, bisa shawarar "Ziri daya da hanya daya", da tsarin dandalin tattaunawar hadin kai tsakanin Sin da Afirka, kasashen Kenya da Sin na karfafa cudanya da hadin kai ta fuskar tattalin arziki da cinikayya. Ya bada Misalin cewa, cimma nasarar gina hanyar dogo ta Mombasa-Nairobi ya sa kaimi ga saurin ci gaban kasar Kenya a fannonin sufuri da jigilar kayayyaki da kuma cinikayya. A daya bangaren kuma, ya samar da guraban aikin yi sama da dubu 50 a wurin.

A nasa bangaren, Deo Kamagi daga jaridar Daily News ta kasar Tanzaniya shi ma ya nuna cewa, ci gaban kasashen Afirka na bukatar goyon bayan kasar Sin a fannonin kudi da fasaha da kuma hazaka. Ya ce tsarin dandalin tattaunawar hadin kai tsakanin Sin da Afirka da shawarar "Ziri daya da hanya daya" sun samar da dama da manufar samun ci gaba ga kasashen Afirka a lokacin da ya dace. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China