Mai magana da yawun hukumar ba da agajin gaggawa ta kasar wato NEMA, Sani Datti, ya shedawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, 'yan kunar bakin waken biyu sun gamu da ajalinsu ne a lokacin da boma boman dake jikinsu suka tarwatse a dai dai lokacin da suke yunkurin kutsawa cikin kasuwar Monday market dake tsakiyar birnin Maiduguri.
Kakakin hukumar ya ce, mutane 17 sun samu raunuka kuma tuni aka garzaya da su asibitin kwararru na garin Maiduguri domin basu kulawa, kana ma'aikatan ceto da jami'an tsaro sun killace wajen da lamarin ya faru.
Ita dai kasuwar ta Monday market, ta sha fuskantar hare haren kunar bakin wake musamman a lokacin da rikicin Boko Haram ya yi kamari a birnin na Maiduguiri, lamarin da ya haddasa salwantar rayukan daruruwan jama'a.(Ahmad Fagam)