in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ronaldinho ya koma Barcelona
2016-09-07 19:20:04 cri
Dan wasan kasar Brazil mai shekaru 36, Ronaldinho ya koma Barcelona da taka leda, sai dai ba'a matsayin dan wasa ba. Dan wasan wanda ya taimakawa kungiyar har ta komawa hayyacinta tsakanin shekarar 2003 zuwa ta 2008, zai kasance a matsayin jakadan kulob din a wannan karo.

Dan wasan na Brazil, wanda ya samu matsayi na bajinta a Camp Nou, bayan da ya taimakawa Blaugrana ta dawo da matsayinta, a wannan karo ma zai sake yin aiki tare da kungiyar. An ce, Barcelona ta bude wani sabon ofis a birnin New York na kasar Amurka a ranar 6 ga watan Satumba, domin neman kara samun karbuwa a duniya, hakan ne ya sa suka sake dawo da Ronaldinho.

Ana sa ran kungiyar wasan zata amsa sunanta, matukar hasashen da aka yi game da Ronaldinho ya kai ga nasara, a yayin da zai yi matukar kokarin tallafawa kolub din kamar yadda ya yi a baya.(Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China