in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan taron koli na G20 zai sa kaimi ga farfado da tattalin arziki da kyautata tsarin raya tattalin arzikin duniya
2015-11-10 10:59:29 cri
Jaridar People's Daily ta fida wani sharhi mai taken "Sin za ta samar da gudummawa wajen kyautata tsarin raya tattalin arzikin duniya" a yau Talata, wanda cikin sa ta bayyana cewa kasar Sin na fatan taron koli na G20 dake gudana a birnin Antalya, zai baiwa duniya kwarin gwiwa, da imani wajen samun damar bude kofa ga juna, da daukar nauyi, da kyautata tsare-tsare, na samar da gudummawar sa kaimi ga farfado da tattalin arzikin duniya, da bunkasuwarsa, da kuma kyautata tsarin raya tattalin arzikin duniya.

Sharhin ya bayyana cewa, a tsakiyar watan Nuwanba, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai tashi zuwa birnin Antalya dake kasar Turkiya, domin halartar taron koli karo na 10 na G20.

Kungiyar G20 tana shafar rayuwar kashi 2 cikin 3 na al'ummar duniya, wadanda yawan tattalin arzikin su ya kai ga kashi 90 cikin dari na al'ummar duniya. Kaza lika cinikayyar wannan kaso ta kai kashi 80 cikin dari na al'ummar duniya. Tana kuma kunshe da manyan kasashe masu ci gaba, da sabbin kasashen da suka fi samun bunkasuwar tattalin arziki a duniya, ta kuma kasance tsarin hadin gwiwar tattalin arziki a tsakanin kasa da kasa na farko, mai kunshe da kasashe masu ci gaba, da kasashe masu tasowa suka shiga, inda suke tsaida kuduri cikin adalci. Don haka kungiyar G20 ke taka muhimmiyar rawa wajen sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China