![]() |
|
2020-11-05 14:56:30 cri |
Yayin taron kuma, mataimakin ministan harkokin wajen Sin Le Yucheng, ya bayyana ra'ayin kasar Sin kan zaben shugaban kasar Amurka da kuma tasirinsa kan dangantakar Sin da Amurka.
A cewarsa, har yanzu ba a kai ga fitar da sakamakon zaben ba, yana mai fatan za a kammala ba tare da wata tangarda ba. Ya ce kyautata dangantakar Sin da Amurka ba muradi ne na kasashen biyu da al'ummominsu kadai ba, har ma da daukacin al'ummar duniya.
Ya kara da cewa, yana fatan sabuwar gwamnatin Amurka za ta hada hannu da Sin, wajen daukaka dangantakarsu ta hanyar zaman lafiya ba tare da fito na fito ba, bisa mutuntawa da moriyar juna da kuma mayar da hankali kan hadin gwiwa da hukuri da juna da ingiza dangantakar bisa turba madaidaiciya. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China