Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kafafen yada labaran Sin da Afrika sun bukaci a kara hadin gwiwa yayin da ake fama da annobar COVID-19
2020-10-29 10:18:48        cri
Wakilai daga kafafen yada labaran kasar Sin da na kasashen Afrika a ranar Laraba sun bukaci a karfafa hadin gwiwa domin kalubalantar masu neman siyasantar da batutuwan dake shafar annobar COVID-19.

Wakilan sun bayyana hakan ne a wani taron kafafen yada labarai da suka gudanar ta intanet a ranar Laraba.

A cewar wakilan, ya kamata kafafen yada labaran su yayata hadin gwiwar da Sin da Afrika ke yi a kokarin kawar da annobar, kuma su bayar da gudunmawa wajen farfadowar harkokin tattalin arziki, da kyautata rayuwar al'umma a kasashe masu tasowa bayan annobar.

Taron ya cimma matsayar cewa, kafafen yada labarum za su rungumi tsarin cudanyar bangarori daban daban da kuma gudanar da harkokin su bisa tsarin manufar MDD, kana za su cigaba da goyon bayan hukumar lafiya ta duniya WHO a kokarin yaki da annobar COVID-19.(Ahmad)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China