2020-09-10 13:20:53 cri |
Yau Alhamis 10 ga watan nan, rana ce ta malamai ta kasar Sin, wadda aka fara gudanar da bikinta tun daga shekarar 1985. Shugabannin kasar Sin, da dalibai da ma sauran al'ummar Sin, na amfani da ranar wajen jinjinawa gudummawar malamai a dukkanin matakan ba da ilimi.
Da yake yanzu kasar Sin na kara bude kofar ta ga kasashen ketare, karin malamai daga sassan duniya na shigowa kasar ta Sin, domin ba da gudummawar su a fannonin samar da ci gaba daban daban. Malam Haruna Muhammad Sani daga jamhuriyar Kamaru, na daga cikin irin wadannan malamai, yana kuma malanta a jami'ar koyar da harsunan kasashen waje ta lardin Hebei a arewacin kasar Sin.
A saurari tattaunawar da wakilinmu Saminu Alhassan ya yi tare da shi dangane da aikin da ya gudanar a nan kasar Sin.
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China