Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Zargin ana hana 'yancin addini a jihar Xinjiang ba shi da tushe
2020-08-28 14:07:57        cri
Jiya Alhamis, ofishin watsa labarai na gwamnatin jihar Xinjiang mai cin gashin kanta ta kasar Sin, ya kira wani taron manema labarai, inda shugaban kwamiti mai kula da batun kabilu, Mahmouti Wusman ya bayyana cewa, wasu labarai da kafofin watsa labarai na kasashen ketare suka yada, cewar, wai ana hana 'yancin addini, da kuma cin zarafin musulmai a jihar Xinjiang ba su da tushe.

Ya ce, tsarin mulkin kasar Sin ya nuna cewa, dukkanin al'ummomin kasar Sin suna da 'yancin bin addini, kuma jihar Xinjiang ta tsara manufofin dake shafar 'yancin addini, ana kiyaye aikace-aikacen addinai bisa dokoki, kuma ba wani mutum ko wata kungiya, da za su iya tsoma baki cikin wadannan harkoki.

Cikin taron, shugaban ofishin sarrafa albarkatun kwadago, da tabbacin zaman al'umma na jihar Xinjiang, Rehemanjiang Dawuti, ya bayyana cewa, zargin wai ana tilastawa al'ummomin jihar yin aiki, labari ne na jabu, wanda wasu kafofin watsa labarai na yammacin duniya suka kirkira.

A nasa bangare kuwa, shugaban ofishin ba da ilmi na jihar Parhati Izmu, ya ce ba a taba tilastawa dalibai zama a makarantu ba, kuma labaran da kafofin watsa labaran kasar Amurka suka fidda, cewar, wai tsarin ba da ilmi, tare da tilastawa dalibai zama a makarantu na jihar Xinjiang, ya raba yara da iyayensu, wannan labari karya ce kawai, wadda aka tsara domin bata sunan kasar Sin. (Maryam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China