Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Xi ya mika sakon ta'aziya ga takwaransa na Lebanon kan fashewar da ta auku a Beirut
2020-08-05 19:37:08        cri

Shugaban kasar Sin Xi jinping, ya aikawa takwaransa na kasar Lebanon Michel Aoun sakon ta'aziya Larabar nan, dangane da mummunar fashewar da ta auku a Beirut, fadar mulkin kasar Lebanon.

A cikin sakon, shugaba Xi ya ce ya kadu da samun labarin fashewar da ta auku a Beirut, wadda ta yi sanadiyar rayuka da dama.

A madadin gwamnatin kasar Sin da al'ummar Sinawa, da shi kansa, Xi ya mika sakon ta'aziya ga iyalan wadanda lamarin ya rutsa da su, tare da jajantawa iyalan wadanda suka jikkata da fatan samun sauki cikin gaggawa ga wadanda suka jikkata.(Ibrahim)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China