Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Masanin Birtaniya: Tattalin arzikin Sin zai kara taka rawa a duniya
2020-07-17 20:40:37        cri

Alkaluman tattalin arzikin kasar Sin a rubu'i na biyu na shekarar bana, da hukumar kididdigar kasar ta fitar a jiya Jumma'a sun jawo hankalin kasa da kasa, inda shahararren masani kan harkokin kasar Sin dan kasar Birtaniya Martin Jacques ke ganin cewa, karuwar tattalin arzikin kasar Sin a rubu'i na biyu na shekarar nan, na nuna karfin ci gaban tattalin arzikin kasar.

Martin Jacques ya kara da cewa, a rubu'in farko na bana, tattalin arzikin kasar Sin ya ragu da kaso 6.8 bisa dari, idan aka kwatanta da na makamancin lokaci a bara, amma a rubu'i na biyu, adadin ya karu da kaso 3.2 bisa dari, lamarin da ya bai wa al'ummun kasa da kasa matukar mamaki, kana ya nuna cewa, gwamnatin kasar Sin na da karfi matuka a fannin tafiyar da harkokin kasa.

Masanin ya kara da cewa, tun bayan rikicin hada-hadar kudi a fadin duniya a shekarar 2008, tattalin arzikin kasar Sin ya ci gaba da taimakawa sosai ga ci gaban tattalin arzikin duniya, kuma yanzu haka annobar COVID-19 tana bazuwa a sauran sassan duniya, yayin da tsarin tattalin arzikin duniya shi ma ya sauya, don haka kasar Sin za ta taka karin rawar gani, wajen ci gaban tattalin azikin duniya. (Jamila)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China