Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sin za ta hada kai da al'ummomin kasa da kasa don inganta rayuwar al'ummomin duniya
2020-06-23 20:11:22        cri

Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Zhao Lijiang, ya bayyana kudirin kasarsa na yin aiki tare da al'ummomin kasa da kasa, a wani mataki na ganin an aiwatar tsarin kasancewar bangarori daban-daban, da cimma manufar raya da kare hakkin dan-Adam, da inganta rayuwar al'ummomin kasashen duniya.

Ya ce, jiya ne, hukumar kare hakkin dan-Adam ta MDD ta sake amincewa da wani kudiri kan "bunkasa alakar cin moriyar juna a fannin kare hakkin dan-Adam", kudirin da kasar Sin ta gabatar, don mayar da martani kan tambayoyin da aka gabatar kan wannan batu.(Ibrahim)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China