![]() |
|
2020-06-20 17:26:01 cri |
Hukumomi a jihar Xinjiang na nuna kwazo wajen samar da tabbaci ga mabiya addinin Musulunci don su gudanar da harkokin ibada yadda ya kamata, da maida hankali sosai ga karewa gami da gyara masallatai daban-daban, kuma akwai wasu masallatai a jihar wadanda aka gina su a shekarun 1980 zuwa 1990. Sakamakon ci gaban birane da garuruwa gami da bunkasuwar yankunan karkara, gwamnatin jihar Xinjiang tana kokarin daukar matakai daban-daban domin sake gyara wasu masallatai, wadanda suka riga suka tsufa ko suka lalace, domin biyan bukatun mabiya addinin Musulunci, da saukaka musu ayyukan ibada da salloli, al'amarin da ya samu babbar karbuwa daga malaman bangaren addini gami da mabiya addinin Musulunci a wurin.(Murtala Zhang)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China