Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kasar Sin Za Ta Kara Hadin Kai Tare Da Sauran Kasashe A Fannin Nazarin Allurar Rigakafin COVID-19
2020-06-07 16:38:33        cri

Ofishin watsa labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin ya kira taron manema labaru a Lahadi don gabatar da wata takardar bayani dangane da matakan da kasar Sin ta dauka a kokarin dakile cutar COVID -19. Inda Wang Zhigang, ministan kimiyya da fasaha na kasar Sin, ya jaddada bukatar hadin gwiwa tsakanin bangarorin kasa da kasa, a yunkurin samar da allurar rigakafin cutar.

A cewarsa, wannan hadin gwiwa zai shafi aikin nazari, gami da gwaje-gwajen amfani da allurar. Sa'an nan bayan da aka gama nazarin allurar, kasar Sin za ta samar da rigakafin kyauta ga kasashe daban daban, a matsayin wani magani na jama'a. (Bello Wang)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China