Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Adadin mutanen da COVID-19 ta kashe a Afrika ya zarce 3,200 bayan mutane 107,000 sun harbu da cutar
2020-05-25 11:28:26        cri

Jimillar adadin mutanen da aka tabbatar sun kamu da cutar COVID-19 a fadin nahiyar Afrika ya karu daga 103,933 a ranar Asabar zuwa mutane 107,412 ya zuwa safiyar ranar Lahadi, cibiyar dakile cutuka masu yaduwa ta Afrika, wato (Africa CDC) ta sanar da hakan a ranar Lahadi.

Hukumar dake yaki da annobar a nahiyar ta bayyana cewa, kawo yanzu, cutar ta riga ta yadu a kasashen Afrika 54, kana hukumar ta kara da cewa, ya zuwa safiyar Lahadi mutane 42,626 sun warke bayan kamuwa da cutar ta COVID-19.

A cewar Africa CDC, adadin mutanen da cutar COVID-19 ta kashe a fadin nahiyar Afrika ya karu daga 3,183 a safiyar ranar Asabar, zuwa mutane 3,246 a safiyar ranar Lahadi.

Cibiyar dakile yaduwar cutukan ta Afrika ta ce, shiyyar arewacin Afrika ne annobar COVID-19 ta fi yiwa illa a duk fadin nahiyar ta fuskar yawan adadin mutanen da suka kamu da cutar da kuma wadanda suka mutu a sanadiyyar cutar.(Ahmad Fagam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China