Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Ma'aikatar wajen Sin: Baza jita-jita ba zai kashe kwayar cuta ba
2020-05-14 21:41:33        cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Zhao Lijian ya bayyana yau Alhamis a yayin taron ganawa da manema labarai a nan birnin Beijing cewa, baza jita-jita ba shi ne zai kashe kwayar cuta ba, shafawa wasu bakin fenti shi ma ba zai dakile annoba ba.

Kalaman nasa na zuwa ne, yayin da Amurka ta sanar da cewa, masu satar bayanai ta yanar gizo na kasar Sin sun sace bayanan hukumomin nazarin kwayar cutar COVID-19 na kasar. Zhao ya kara da cewa, kasar Sin tana adawa da matakan Amurka na shafa mata bakin fenti, yana ganin cewa, a daidai lokacin da ake kokarin dakile annobar a fadin duniya, bai dace a kawo batun dora laifin satar bayanai ta yanar gizo ba.(Jamila)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China