2020-04-30 21:14:44 cri |
Dangane da maganar da sakataren harkokin wajen kasar Amurka Mike Pompeo ya fada kuwa, don neman matsawa kasar Sin lamba ta yarda da wani bincike, kan cibiyar nazarin kwayoyin cuta ta birnin Wuhan, mista Geng Shuang ya bukaci dan siyasar na kasar Amurka, da ya daina yunkurin dora wa kasar Sin laifi.
Ban da wannan kuma, game da tasirin da annobar COVID-19 ka iya haifarwa ga tsaron abinci na duniya, Geng ya ce kasar Sin za ta kara hadin kai tare da sauran bangarorin duniya, don tabbatar da tsaron abinci a duniya baki daya. (Bello Wang)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China