Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Masanin tattalin arzikin Amurka: Managartan manufofin tattalin arzikin sun kara farfadowar tattalin arzikin Sin
2020-04-27 13:43:48        cri
Tun bayan samun nasarar kandagarki da kuma dakile annobar COVID-19 a kasar Sin, yanzu dukkan fannoni sun dawo bakin aikinsu a kasar. Wani masanin tattalin arzikin Amurka yayi amanna cewa, managartan manufofin da gwamnatin kasar Sin ta aiwatar sun tabbatar da saurin farfadowar tattalin arzikin kasar kuma akwai yiwuwar zai cigaba da samun bunkasuwa yadda ya kamata.

William, babban jami'in cibiyar nazarin tattalin arziki ta Milken Institute ta kasar Amurka, yace kasar Sin itace kasa ta farko a duniya da ta kai ga dakile annobar covid-19, kuma ta dauki matakai akan lokaci kana ta aiwatar da manufofin bunkasa tattalin arzikinta, ya kara da cewa, yana da kwarin gwiwa game da bunkasuwar tattalin arzikin Sin a watanni shida na karshen wannan shekarar.

William ya ce, a ganin masana tattalin arzikin Amurka, tattalin arzikin Amurka zai ja da baya a rubu'i na biyu da na uku na wannan shekarar, yace ya kamata Amurka ta yi koyi daga kasar Sin game da matakan farfado da tattalin arzikinta.

David uribe, shehun malami a jami'ar jahar California, yayi imanin cewa, rashin samun hadin kai tsakanin gwamnatin tarayyar da kananan hukumoimn jahohin Amurka ya sa sun rasa samun damar dakile annobar COVID-19 a kasar. Yadda kasar Sin ta farfado da sana'o'i daban daban bayan da ta dakile yaduwar cutar, ya kuma shaida karfi da ingancin tattalin arzikin kasar wajen tinkarar matsaloli.(Ahmad)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China