Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Xi ya kira al'ummun kasarsa da su jure wahalhalu tare yayin rangadin aikinsa a Shaanxi
2020-04-25 20:48:08        cri
A shekarun 1950, mahukuntan gwamnatin kasar Sin a wancan lokaci sun tsai da kudurin kaura da jami'ar Jiaotong daga birnin Shanghai dake gabar teku zuwa birnin Xi'an, fadar mulkin lardin Shaanxi dake yammacin kasar, domin goyon bayan ci gaban tattalin arziki da zaman takewar al'umma a yankin yammacin kasar, gaba daya malamai sama da 1400 da dalibai fiye da 3000 ne suka tashi daga Shanghai domin fara karatunsu a Xi'an. A cikin shekaru 60 da suka gabata, malamai da dalibai na jami'ar Jiaotong ta Xi'an sun taka babbar rawa kan gine-ginen kasar Sin, kamar yadda tsohon firayin ministan Faransa Jean-Pierre Raffarin ya bayyana, wadannan malamai da dalibai dukiyoyi ne mafi daraja na kasar Sin.

Kwanan baya shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ziyarci jami'ar Jiaotong ta Xi'an, inda ya bukaci malamai da daliban jami'ar su koyi hali na gari na tsoffin malaman jami'ar, haka kuma su taka rawa a sabon zamanin da ake ciki.

Shugaba Xi ya ce, muhimmiyar ma'anar kaura daga Shanghai zuwa Xi'an ita ce kishin kasa, shi ne kuma dalilin da ya sa kasar Sin ta samu ci gaba cikin sauri a cikin shekaru sama da goma da suka gabata.

Yanzu haka ana yaki da annobar cutar numfashi ta COVID-19, hali na gari yana kara karfafa wa ma'aikatan jinya da daliban da suka kammala karatu daga jami'o'i da kuma sauran al'ummun kasar zuciya yayin da suke fuskantar kalubalen. Kamar yadda babban darektan hukumar lafiya ta duniya Tedros Adhanom Ghebreyesus ya bayyana, ma'aikatan jinya dake cikin asibitocin kasar Sin jarumai ne na gaske, saboda sun shirya sadaukar da rayukansu domin tabbatar da tsaron duniya.

A daya bangaren, yayin da ake yaki da talauci, halin na garin yana karfafa wa al'ummun kasar Sin gwiwa, har ya sa kasar Sin ta cimma burin kubutar da matalauta sama da miliyan 800 daga kangin talauci a cikin shekaru 70 da suka gabata, wato tun bayan da aka kafa sabuwar jamhuriyar jama'ar kasar Sin a shekarar 1949.

Yanzu annobar tana ci gaba yaduwa cikin sauri a fadin duniya, har ta gurgunta ci gaban tattalin arziki, a don haka, shugaba Xi ya sake nanata halin na gari na kaura daga yanki mai ci gaba zuwa yanki mai tasowa, domin tunatar da al'ummun kasar cewa, dole ne a kara yin kokari domin samun nasara ta karshe, a sa'i daya kuma, zai ingiza kasar ta cimma muradun ci gabanta na bana bisa shirin da aka tsara, tare kuma da gina zaman takewar al'umma mai matsakaicin wadata a kasar daga duk fannoni.(Jamila)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China