![]() |
|
2020-04-16 10:15:36 cri |
Galibin 'yan kasashen ketare da suka halarci taron su ne daliban dake karatu a binrin Guangzhou, wasu kuma suna aiki a birnin, wadanda suka zo daga kasashen Japan, Australia, Somaliya, Nijeriya, Malawi da kuma Ghana da sauransu.
A yayin zantawar tasu, Zhong Nanshan ya yi musu cikakken bayani kan yadda kasar Sin take yaki da cutar numfashi ta COVID-19. Ya ce, kasar Sin ta dauki matakai masu karfi, kamar killace birane, gabatar da bayanai ga al'umma ba tare da boye kome ba, da kuma kafa tsarin hadin gwiwar yin kandagarki da dalike yaduwar annobar, domin hana yaduwar cutar numfashi ta COVID-19 a kasar baki daya.
Haka kuma, ya ce, barkewar annobar ya zama darasi ga dukkanin kasashen duniya, ya kamata mu kara saninmu game da duniyar da muke zama cikinta, da kuma yin hadin gwiwa wajen yaki da cutar. (Maryam)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China