![]() |
|
2020-04-15 20:20:24 cri |
Zhao ya bayyana haka ne yayin taron manema labarai, yana mai cewa, Sin da Afirka abokan juna ne na kwarai na dogon lokaci komai wahala ko dadi. A lokacin da kasar Sin ta shiga lokaci mai tsanani na yaki da COVID-19, kasashen Afirka sun nuna mata goyon baya, kuma kasar Sin ba za ta taba mantawa ba.
Ya ce, kasar Sin tana mayar da hankali kan yanayin cutar a nahiyar Afirka, har ma ta samarwa AU da dukkan kasashen nahiyar da cutar ta bulla a kasashensu taimakon kayayyakin yaki da cutar da ake bukata rukuni-rukuni.(Ibrahim)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China