![]() |
|
2020-03-22 17:09:01 cri |
Firaministan kasar Scott Morrison ya zanta da gidan rediyon 2GB a kwanan nan ya bayyana cewa, kimanin kaso 80% daga cikin mutanen da aka tabbatar sun kamu da cutar COVID-19 a Australiya, sun shigo kasar ne daga sauran sassan duniya, ko kuma sun taba yin mu'amala kai-tsaye da wadanda suka shigo kasar daga ketare, kana, akasarinsu daga Amurka ne. Morrison ya kara da cewa, a ra'ayinsa, babu wata alamar dake nuna cewa duk wata kasa, ciki har da kasar Sin, ta aikata wani abu da gangan.
Kafofin watsa labarai da dama sun bayyana irin wannan furucin na Morrison a matsayin suka ga gwamnatin Donald Trump saboda sakacin da ta yi wajen dakile yaduwar cutar. Kwararru da masana daga bangaren lafiya da gwamnatin kasar Australiya sun nuna cewa, har yanzu ba a kai ga mataki mafi muni na yaduwar COVID-19 a Australiya ba. Kuma bisa hasashen da aka yi, zuwa lokaci mafi muni, za'a samu mutane miliyan 15 wadanda suka kamu da cutar, kuma yawan mace-macen da za'a samu zai iya kaiwa dubu 150, har ma za'a dauki akalla rabin shekara ana fama da annobar a kasar ta Australiya. (Murtala Zhang)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China