![]() |
|
2020-03-09 10:18:46 cri |
Wani jami'in hukumar tsaron kasar Nijer ya bayyana cewa, sansanin da aka kai wa harin, na lardin Diffa dake kudu maso gabashin kasar Nijer. A wannan rana, dakarun kungiyar Boko Haram sun shiga kasar Nijer daga yankin iyakar dake arewa maso gabashin Nijeriya, sa'an nan sun yi musayar wuta da sojojin wannan sansanin na Nijer, lamarin da ya haddasa rasuwar a kalla mutane 8, ciki har da wani kwamandan soja daya da sojoji da dama. Haka kuma, dakarun sun kwashe wasu motoci da makamai daga sansanin.
Yanzu, an riga an kai sojojin da suka ji rauni asibitin dake kusa da sansanin. Kana, ya zuwa yanzu, gwamnatin kasar Nijer ba ta fidda sanarwa kan wannan batu ba. (Maryam)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China