2020-03-08 17:12:59 cri |
Misali likitocin kasar Sin sun hada wasu magungunan gargajiyar kasar Sin tare, domin kyautata gudanar aikin huhun mutanen da suka kamu da cutar, haka kuma sun samu sakamako a bayyane.
A cikin 'yan kwanakin da suka gabata, gwamnatin kasar Sin ta tura likitocin gargajiyar kasar Sin sama da 5000 zuwa lardin Hubei, inda cutar ta fi kamari, har sun samar da magungunan sha na gargajiyar kasar ga mutanen da suka kamu da cutar kaso 75 bisa dari, a sauran sassan kasar kuwa, sun samar da magungunan ga mutanen da suka kamu da cutar kaso 90 bisa dari.
A ranar 6 ga wata, mambar tawagar ba da jagoranci kan aikin yakar cutar ta kwamitin tsakiya na JKS kuma mai kula da hukumar lafiya ta kasar Sin Yu Yanhong ta bayyana cewa, kawo yanzu mutanen da suka kamu da cutar sama da dubu 50 sun riga sun warke, yawancinsu sun taba shan magungunan gargajiyar kasar Sin.(Jamila)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China