Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Jami'in WHO ya yabawa tallafin Sin wajen dakile cutar COVID-19
2020-03-08 16:15:26        cri
Babban jami'in hukumar lafiya ta duniya (WHO) Tedros Adhanom Ghebreyesus ya yabawa kasar Sin bisa bayar da gudunmowar dala miliyan 20 ga hukumar ta WHO domin yakar annnobar cutar numfashi ta COVID-19 a duniya da tallafawa kasashe masu tasowa wajen farfado da ayyukan kandagarkin cutar.

Tedros ya bayyana hakan ne a lokacin ganawa da Chen Xu, wakilin din din din na kasar Sin a ofishin MDD dake Geneva (UNOG).

Ya bayyana farin cikinsa da kuma nuna yabo ga gwamnatin kasar Sin, wacce take kokarin magance wahalhalun da take fuskanta, bisa jin kan da ta nuna wajen tallafawa kasashe masu tasowa a wannan matsanancin yanayin da ake ciki na yaki da annobar a duk duniya.

Mista Tedros ya ce, hukumar WHO za ta ci gaba da yin aiki tare da kasar Sin domin ingiza ayyukan hadin gwiwa tsakanin kasa da kasa wajen magancewa da kandagarkin cutar.

A lokacin ganawar, Chen ya ce, ayyukan magancewa da kandagarkin cutar COVID-19 a kasar Sin yana samun gagarumar nasara da kuma kyakkyawan sakamako bisa ingantattun matakan da gwamnatin Sin da al'ummar kasar suke dauka.

Kwayar cutar tana shafar daukacin kasashen duniya, in ji wakilin na kasar Sin, ya kara da cewa, kasar Sin za ta ci gaba da yin hadin gwiwa da hukumar WHO da kuma dukkan bangarori waje yakar annobar cutar.(Ahmad Fagam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China