2020-03-04 10:53:15 cri |
Hukumar lafiya ta kasar Sin, ta ce mutane 119 ne aka tabbatar sun kamu da cutar numfashi ta COVID-19 a jiya Talata, kana wasu 38 suka rasu bayan sun sha fama da ita a sassan kasar ta Sin.
Cikin wadanda cutar ta hallaka dai, akwai mutane 37 a lardin Hubei, da mutum guda a yankin Mongolia ta gida mai cin gashin kan sa. A daya bangaren kuma, an gabatar da jerin mutane 143, da ake aikin tantance ko sun kamu da cutar ko a'a. (Saminu)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China