Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Jakadan Sin a Najeriya ya ziyarci cibiyar nazarin manufofi da manyan tsare-tsaren Najeriya
2020-02-28 12:04:38        cri

Jakadan kasar Sin dake Najeriya, Mista Zhou Pingjian, ya ziyarci cibiyar nazarin manufofi da manyan tsare-tsaren kasa dake garin Kurun jihar Filato a jiya Alhamis, inda ya yi shawarwari da shugaban cibiyar, shehun malami Habu S. Galadima, tare da kaddamar da sashin nazarin harkokin kasar Sin a cibiyar. Haka kuma, Jakada Zhou ya yi jawabi ga mahalarta taron karawa juna sani da ma'aikatan cibiyar kan manufofin kare hakkin dan Adam gami da kwarewar kasar a fannin daukar ma'aikata.

A nasu jawabin, mahalarta taron, sun jinjina kwararan matakan da gwamnatin kasar Sin ta dauka na shawo kan cutar numfashi ta COVID-19, da babbar gudummawa da sadaukarwar da kasar ta bayar ga inganta harkokin kiwon lafiyar duniya baki daya. Sun kuma bayyana cewa, gwamnati gami da jama'ar tarayyar Najeriya na zama kafada da kafada da kasar Sin, suna kuma da yakinin cewa Sin za ta iya shawo kan annobar cutar nan da nan.

Har wa yau, sun ce, kasar Sin ta yi abin al'ajabi wajen samun ci gaba ta hanyar shugabanci nagari da tsarin kasar mai inganci, inda a ganinsu, tsayawa kan daidaita matsaloli bisa hakikanin halin da ake ciki a kasar ita ce mafita. Najeriya na fuskantar matsalolin da suka kunshi yawan jama'a da kuma rashin samun guraban ayyukan yi, a don haka ya kamata ta koyi wasu dabarun kasar Sin a fannonin da suka shafi inganta rayuwar al'umma, da raya sana'o'in dake bukatar daukar ma'aikata masu yawa, da kuma kara bada fifiko kan samar da guraban ayyukan yi ga al'ummar kasar.(Murtala Zhang)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China