![]() |
|
2019-11-13 20:38:48 cri |
A yayin ganawar, Nasiru Yusuf Gawuna ya yi bayani game da ziyarar da ya kai a lardin Shandong na kasar Sin, a cewarsa, Allah ya albarkaci jihar Kano da yawan al'umma, da albarkatu, tana kuma da makomar bunkasuwa a nan gaba, wadda ta kasance wurin da kamfanonin kasar Sin ki ribibin zuwa a arewacin Najeriya. Ya ce, jiharsa na son kara kyautata yanayin zuba jari, da nufin kara jawo hankulan kamfanonin kasar Sin don su zuba jari a jihar, ta yadda za a cimma burin samun moriya da nasara tare.
A nasa bangaren, jakada Zhou Pingjian ya nuna godiya ga gwamnatin jihar Kano kan yadda ta saukaka Sinawa dake jihar a fannonin gudanar da ayyuka da ma zama a wurin, ya kuma bayyana cewa, yin cudanya da hadin kai a tsakanin kananan hukumomi, wani muhimmin sashe ne na kyakkyawan hadin kai a tsakanin kasashen Sin da Najeriya, kasar Sin na fatan karfafa cudanya da hadin kai tare da bangaren Najeriya a fannonin samar da kayayyaki, al'adu, yawon shakatawa, aikin gona da kuma masana'antun kere-kere, kana ya bayyana fatansa na ganin Najeriya ta kara kyautata muhallin gudanar da cinikayya, don kara jawo hankulan masu zuba jari na kasar Sin. (Bilkisu)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China