Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Xi Jinping ya aike da sakon taya murnar bude taron kolin AU karo na 33
2020-02-09 21:01:36        cri
Yau Lahadin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aike da sako ga taron shugabanni kungiyar tarayyar kasashen Afrika (AU), karo na 33 don taya murna ga kasashe da jama'ar nahiyar Afirka.

A cikin sakonsa, Xi Jinping ya jaddada cewa, yanzu dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen Afirka na cikin wani lokaci mafi kyau a tarihi. Bisa yanayin sauye-sauye da duniya ke ciki, karfafa gina al'umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya a tsakanin Sin da Afirka na dacewa da moriyar bai daya ta jama'ar bangarorin biyu. Kasar Sin zata ci gaba da tabbatar da nasarorin da aka cimma a gun taron kolin na dandalin tattaunawar hadin kai a tsakanin Sin da Afirka da aka shirya a Beijing a dukkan fannoni, da kuma gaggauta raya shawarar "Ziri daya da hanya daya" a tsakaninsu, don kara bada gudummowa wajen bunkasa da farfado da Afirka, da kara samar da alheri ga jama'ar sassan biyu. (Bilkisu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China