![]() |
|
2020-02-09 15:55:33 cri |
Hukumar ta kara da cewa yawan sabbin mutanen da ake zaton sun kamu da cutar ya tasamma 3,916 ya zuwa ranar Asabar.
Kana ya zuwa ranar Asabar din yawan marasa lafiyar dake cikin matsanancin hali ya kai 87, yayin da aka sallami sabbin yawan mutane 600 bayan sun warke daga annobar.
Baki dayan adadin mutanen da suka kamu da cutar a fadin kasar Sin sun kai 37,198 ya zuwa karshen ranar Asabar, a cewar hukumar lafiyar, yayin da jimillar mutanen da annobar ta hallaka a fadin kasar ya kai 811.
Sai kuma majinyata 2,649 da aka sallama daga asibiti bayan sun warke daga cutar.
Ya zuwa karshen ranar Asabar, mutane 26 ne aka tabbatar sun kamu da cutar a yankin musamman na Hong Kong, 10 a yankin Macao sai mutane 17 a yankinTaiwan.
Majinyaci guda daga yankin Macao da wani guda daga yankin Taiwan an sallamesu daga asibiti bayan sun murmure daga cutar. (Ahmad)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China