Kasar Sin tana kokarin gwada wasu magungunan annobar cutar numfashi
Sun Yanrong, mataimakiyar darekta a sashen kula da halittu na ma'aikatar kimiyya da fasaha ta kasar Sin ta bayyana a yayin taron manem labaru da hukumar kiwon lafiyar kasar Sin ta shirya yau Talata cewa, an samu ci gaba wajen yin nazari kan annobar cutar numfashin da ta bulla a kasar, musamman ma a fannin nazarin magani. Yanzu haka an zabi wasu magungunan yakar annobar, ana nan kokarin gwada su wajen shawo kan annobar da ta bulla. (Tasallah Yuan)
Labarai masu Nasaba