Kasar Sin na matukar kokarin kubutad da wadanda suka kamu da annobar cutar numfashi
Jiao Yahui, mataimakiyar shugaban sashen kula da harkokin asibitoci na hukumar kiwon lafiyar kasar Sin ta bayyana a yayin taron manema labaru da aka shirya yau da yamma cewa, hukumar ta dauki wasu matakai masu tsauri don ba da magani ga wadanda suka kamu da annobar cutar numfashi wadanda suke cikin mummunan yanayi, musamman ma a lardin Hubei. Yanzu haka hukumar ta yi amfani da karfin sassa daban daban, a yi matukar kokarin kubutad da karin mutane, da rage yawan masu kamuwa da annobar da yawan mace-mace. (Tasallah Yuan)
Labarai masu Nasaba