![]() |
|
2020-01-03 09:18:23 cri |
Samuel Arrali Kisembo, ya shaidawa kamfanin dillancin labarain Xinhua ta wayar tarho cewa, mutanen sun bi ta tafkin Albert da kasashen biyu ke amfani da shi. Ya ce, suna aiki tare da jagororin yankin, da ofishin firaminista da babban kwamishinan kula da 'yan gudun hijira na MDD, don kai wadannan mutane zuwa cibiyoyin tsugunar da masu kaura dake Sebigoro, duba da yadda ake sa ran Karin mutane za su tsallaka zuwa kasar ta Uganda.
A cewar hukumar kula da 'yan gudun hijra ta MDD, kasar Uganda ita ce kasa ta uku a duniya wajen karbar 'yan gudun hijira. Inda yanzu haka kusan 'yan gudun hijira miliyan 1.36 galibi daga kasashen Sudan ta kudu, da Jamhuriyar demokiradiyar Congo(DRC), da Burundi suke samun mafaka a kasar. (Ibrahim)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China