![]() |
|
2019-12-11 15:54:36 cri |
Zakia Hussein, mataimakiyar kwamishinan 'yan sandan Somali, ta ce jami'an tsaro sun kawo karshen kawanyar da suka yiwa sanannen otel din nan na SYL na tsawon sa'o'i 7, bayan da suka samu nasarar kashe dukkan maharan 5.
Zakia ta fada cikin wata sanarwa cewa, an kawo karshen harin, kuma jami'an tsaro sun kashe dukkan maharan su 5, ta kara da cewa, sojoji biyu da fararen hula 3 sun rasa rayukansu a sanadiyyar harin.
A cewarta, sojoji biyu da fararen hula 9 sun samu raunuka a lokacin harin na otel, inda maharan suka yi amfani da manyan makamai a kusa da fadar shugaban kasar. (Ahmad)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China