2019-11-30 16:13:55 cri |
Shugaba Xi ya bayyana a cikin bayaninsa cewa, jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin tana jagorantar al'ummun kasar, wajen gwajin manufofi daban daban, cikin shekaru 70 bayan kaddamar da jamhuriyar jama'ar kasar Sin a shekarar 1949, ta yadda sannu a hankali suka kafa tsare-tsare masu halayyar musamman ta kasar Sin, a fannonin siyasa da shari'a. Daga bisani an samu damar kare ci gaban al'ummar kasar Sin, tare da samar da fasahohi masu daraja a kokarin kyautata tsare-tsaren siyasa da na shari'a. A cewar shugaba Xi, kamata ya yi, daukacin 'ya'yan jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin, su yi imani da turbar da suka zaba wajen raya kasa, da tsayawa kan ra'ayoyi, da tsare-tsare, gami da al'adun kasar Sin. Da kuma ci gaba da kokarin raya kasar Sin, bisa manufofin da jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin, da jama'ar kasar suka gabatar. (Bello Wang)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China