2019-11-28 19:03:24 cri |
A jiya ne, Amurka ta zartas da wannan doka, wadda kasar Sin ta yi biris da matukar nuna rashin jin dadinta, domin wannan mataki tsoma baki ne a harkokin cikin gidan kasar Sin, kuma ya keta dokar kasa da kasa da ka'idojin dangantakar kasa da kasa.
Dadin dadawa, sanarwa ta nuna cewa, gwamnatin kasar Sin za ta tsaya tsayin daka don kiyaye 'yanci da tsaron kasa da ma muradun bunkasuwarta, kana za ta nace ga manufar "kasa daya tsarin mulkin biyu ", tana kuma adawa da duk wani yunkuri na yin shisshigi a harkokin yankin Hong Kong. Yunkurin Amurka na hana bunkasuwar kasar Sin ta hanyar tada tsaune tsaye a Hong Kong ba zai yi nasara ba ko kadan, kamar yadda aka bayyana a cikin sanarwar. (Amina Xu)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China