Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
An bukaci a kara zage damtse wajen farfado da tattalin arzikin yankin tsakiyar Afrika
2019-11-23 16:17:20        cri

Shugaban kasar Kamaru, Paul Biya, ya yi kira da a kara zage damtse domin kara raya tattalin arzikin kasashen kungiyar raya yankin tsakiyar nahiyar Afrika.

Paul Biya, ya bayyana yayin bude taron shugabannin kasashe mambobin kungiyar jiya a birnin Yaounde cewa, sauye-sauyen farashin kayayyakin da ake sarrafawa na ci gaba da tasirin a kan tattalin arzikin kasashen, don haka akwai bukatar kara baza komar tattalin arziki fiye da baya. Yana mai cewa kalubalen tsaro na ci gaba da matsawa harkar hada hadar kudi a yankin.

Ya ce buri guda da suke da shi, shi ne gaggauta samun ci gaba don magance halaltattun bukatun al'ummominsu, musammam na matasa a fannin samun ayyukan yi.

Shugaba Paul Biya ya kara da cewa, ci gaban kungiyar ya tsaya ne kan kaso 1.8 a bara, yayin da farashin kayayyaki ya kara hauhawa da kaso 3, baya ga rashin tabbas game da harkokin tattalin arziki, wanda matsalolin cinikayya da na siyasa a yankin suka haifar.

Ya ce a shirye kasashen yankin suke su ci gaba da fafutukar neman nasarori da ci gaba mai dorewa, duk da tangardar da ake gamuwa da su.

A cewar jami'an kungiyar, ana sa ran taron zai fitar da wasu dabarun da za su inganta dunkulewa da bunkasa huldar cinikayya tsakanin kasashe mambobin kungiyar. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China