Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Aikin gina tashar samar da wutar lantarki daga karfin ruwa na Sin zai inganta dangantakar dake tsakanin Sin da Burundi
2019-09-21 16:48:29        cri
Shugaban kasar Burundi Pierre Nkurunziza ya bayyana yayin bikin bude aikin gina tashar samar da wutar lantarki daga karfin ruwa da Sin za ta yi a kasarsa cewa, aikin zai fadada hadin gwiwar dake tsakanin Burundi da Sin, da kuma inganta danganatakar dake tsakanin kasashen biyu.

Shugaba Nkurunziza ya ce, cikin shekaru 56 da kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin Burundi da Sin, sun raya dangantakar dake tsakaninsu, kana Sin ta zama abokiyar hadin gwiwa ta musamman ta kasar Burundi a duniya.

Ministan kula da albarkatun ruwa da makamashi da ma'adinai na kasar Burundi ya bayyanawa 'yan jarida cewa, yawan wutar lantarki da tashar samar da wutar lantarkin za ta samar ya kai mafi yawa bisa adadin wutar lantarki da aka samar a dukkan kasar, wadda kuma ke da muhimmanci sosai wajen raya kasar a nan gaba.

Jakadan Sin dake kasar Burundi Li Changlin ya bayyana cewa, ban da tashar samar da wutar lantarki, Sin tana gudanar da ayyukan bada taimako a fannonin aikin noma, da bada ilmi, da kiwon lafiya da sauransu a kasar Burundi. Ya ce yanzu an shiga lokaci mafi kyau na raya dangantakar dake tsakanin Sin da Burundi, kuma bisa yanayin da ake ciki a kasar Burundi, Sin za ta kara taimakawa kasar Burundi kara karfinta a nan gaba. (Zainab)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China