Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Gamayyar 'yan adawar Sudan ta ayyana Abdalla Hamdok a matsayin firaiministan kasar
2019-08-16 10:29:32        cri

Hadakar kungiyoyin adawar Freedom and Change Alliance ta Sudan sun amince da bayyana sunan Abdalla Hamdok a matsayin wanda za'a nada firaiminista a gwamnatin rikon kwaryar kasar.

A bisa tsarin yarjejeniayar kafa gwamnatin hadaka ta rikon kwaryar da 'yan adawar na Freedom Alliance suka amince da shi, sun yarda a nada Dr. Abdalla Hamdok a makamin firaiministan kasar a tsawon wa'adin shugabancin gwamnatin rikon kwaryar kasar wanda aka tsawaita wa'adin zuwa shekaru uku da wata uku, a cewar kungiyar kwararrun kasar Sudan, wacce babbar jigo ce ta kungiyar Freedom and Change Alliance.

Kungiyar ta yi maraba da zabar Hamdok a matsayin firaiministan kasar, kuma ta tabbatar da yi masa biyayya.(Ahmad Fagam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China