Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sin tana da babbar ma'ana ga ci gaban Rwanda
2019-08-10 17:11:23        cri
Shugabar hukumar kula da harkokin raya kasar Rwanda Clare Akamanzi ta bayyana a birnin Kigali cewa, Sin tana da babbar ma'ana ga ci gaban kasar Rwanda, kuma akwai kyakkyawar makoma kan hadin gwiwar kasashen biyu.

Madam Akamanzi wadda ta halarci dandalin tattaunawa kan harkokin cinikayya na kasa da kasa, da kungiyar hadin gwiwar hukumomi masu zaman kansu ta kasar Rwanda ta karbi bakuncinsa a jiya, ta bayyanawa 'yan jarida cewa, aikin raya kasar Rwanda yana da nasaba da hadin gwiwar dake tsakaninta da kasar Sin, kuma akwai kyakkyawar makoma kan hadin gwiwar kasashen biyu.

Madam Akamanzi ta kara da cewa, Sin tana da karfi a fannonin zuba jari, da yin kirkire-kikire, da kera kayayyaki, da yawon shakatawa da sauransu. Don haka, kasar Rwanda tana son kasar Sin za ta zuba jari gare ta a fannonin samar da kayayyakin amfanin gona, da tufaffi, da kayayyakin gine-gine, da kayayyakin sadarwa da sauransu, kana tana son kara jawo hankalin Sinawa da su je kasar domin yawon shakatawa, da kuma kara fitar da kayayyakinta zuwa kasar Sin.

Shugaban kasar Rwanda da jami'ai da dama su ma sun halarci dandalin tattaunawar, inda wakilai fiye da 700 daga kasashe 23 suka halarta, ciki har da 'yan kasuwa na Sin kimanin 50. (Zainab)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China