2019-08-08 20:39:13 cri |
Mamba a majalisar gudanarwar kasar Sin kana ministan harkokin wajen kasar, Wang Yi ya aikawa takwaransa na kasar Masar Sameh Shoukry sakon ta'aziyya, dangane da mutanen da aka kashe a harin ta'addanci na baya-bayan da aka kai Alkahira, babban birnin kasar ta Masar.
A cikin sakon, Wang ya jajantawa wadanda suka jikkata da ma iyalan wadanda harin ya rutsa da su.(Ibrahim)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China