![]() |
|
2019-07-31 10:39:55 cri |
Zhang Jun, ya ce kasar Sin za ta yi cikakken amfani da damarmakinta a mastayin mambar dindin-din ta kwamitin sulhu na MDD, da girmama ka'idoji da manufofin Majalisar, da kuma shiga a dama da ita cikin harkokin kasa da kasa, da inganta sulhu ta hanyar siyasa da diflomasiyya da kuma bada gudunmuwa ga cimma zaman lafiya a duniya.
Har ila yau, ya ce kasar Sin za ta inganta hadin gwiwa da kasa da kasa domin magance kalubalen da duniya ke fuskanta bisa hanyar da ta dace.
Kafin kira taron manema labarai da 'yan jaridun kasar Sin, Zhang Jun, ya gabatar da takardar nadinsa ga Sakatare Janar na majalisar, Antonio Guterres. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China