2019-07-30 10:04:29 cri |
Cikin wata sanarwa, Antonio Guterres ya yi kira da a kawo karshen hare-hare kan fararen hula, yana mai tabbatar da cewa irin wadanan hare-haren babbar barazana ce ga tsaron bil adama, kana suna keta dokokin jin kai na kasa da kasa.
A wani sakon da ya wallafa a shafinsa na Tweeter a ranar Lahadi, Shugaban hukumar UNHCR Filippo Grandi, ya bayyana harin a matsayin kisan kiyashi, yana mai cewa rashin tsaro na ci gaba da jefa fararen hula cikin mawuyacin hali a yankin, ciki har da mutane miliyan 2 da suka rasa matsugunansu da kuma masu neman mafaka a kasar. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China